IQNA

‘Yar Majalisar ya Mayar Wa Macron Da Martani Kan Furuncinsa Kan  Musulunci

23:57 - September 23, 2018
Lambar Labari: 3483006
Bangaren kasa da kasa, Natalie Goli wata ‘yar majlaisar dokokin kasar Faransa ce wadda ta mayarwa shugaban kasar Emmanuel Macron da martani kan mahangarsa kan musulunci.

 

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, jaridar Alibilad ta kasar Aljeriya ta bayar da rahoton cewa, a lokacin da take gudanar da jawabi a gaban majalisar dattijan Faransa, Natalie Goli ta bayyana furucin Macron na nemen a yi wa addinin musulunci gyaran fsaka a kasar da cewa wuce gona da iri ne.

Ta ce addinin musulunci ba kayan wani mutum ne ko wani wasu ‘yan siyasa ba, a kan musulmin kasar ne kawa suke hakkin yin nazari dangane da abin da yake maslaha a gare su daidai da mahangar addininsu.

Emmanuel Macron dai ya bayyana bukatar ganin an gudanar da wasu sauye-sauye dangane da lamarin musulmi a kasar.

3749185

 

 

 

 

 

captcha